Yanzu yanzu: Zanga-zanga ta barke a Unguwar Kofar Mata dake birnin Kano.

FB IMG 1754139205275

Iyaye mata da yan mata ne suka fito zanga-zangar suna kira a kawo karshen fadan daban dake haddasa asarar rayukan yayansu babu gaira babu dalili.

Yanzu haka dai tuni jami’an tsaro suka isa wajan domin kwantar da tarzoma.

Wannan dai na zuwa ne dai-dai lokacin da alummar unguwar ke alhinin rasa rayukan wasu da ake zargin yan daba da kashewa sakamokon fadan dabar da ya barke a jiya Juma’a.

Masana da dama na dora alhakin wanzuwar fadan daba tsakanin matasa sakamokon rashin aikin yi da kuma karancin ilimi.

Wannan lamari na zuwa ne dai-dai lokacin da gwamnatin Kano ta gabatar da sabbin jami’an da zasu dakile masu sana’ar kwacen waya da kuma fadan daba a fadin jihar.

Hikima Radio

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *