Tsaro: Majalisar dattawa ta amince da kudirin kafa ƴansandan jihohi

FB IMG 1782325828518

Majalisar dattawan Najeriya ta amince da kudirin gyaran kundin tsarin mulki da ke neman kafa rundunar ‘yansandan jihohi a fadin ƙasar.

Sanatoci sun amince da kudirin ne a ranar Laraba bayan nazari da amincewa da sashe-sashe 26 na kudirin a zaman kwamitin dukkan ƴan majalisar.

Kudirin na da nufin samar da tanadin doka da zai bai wa jihohi damar kafawa da gudanar da rundunonin ‘yansandansu tare da ci gaba da wanzuwar rundunar ‘yansandan tarayya.

Amincewar da majalisar ta yi da kudirin na ɗaya daga cikin manyan matakan da ake ɗauka domin sauya tsarin tsaro a ƙasar, yayin da ake sa ran a kammala sauran matakan doka kafin ya fara aiki a hukumance.

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *