Sarkin Musulmi ya ayyana ranar Alhamis a matsayin 1 ga watan Safar 1448AH

FB IMG 1784117370705

Sarkin Musulmi kuma shugaban majalisar koli ta harkokin addinin Musulunci ta Najeriya (NSCIA), Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya ayyana ranar Alhamis 16 ga Yulin 2026 a matsayin ranar farko ta watan Safar na shekarar Hijira ta 1448.

Sanarwar ta fito ne ta hannun Wazirin Sakkwato kuma shugaban Kwamitin ba da Shawara kan harkokin addini na majalisar masarautar Sakkwato, Farfesa Sambo Wali Junaidu.

A cewar sanarwar, Kwamitin ba da shawara kan harkokin Addini tare da Kwamitin kula da ganin wata na kasa ba su samu sahihin rahoton ganin jinjirin watan Safar ba a ranar Talata 14 ga Yulin 2026, wadda ta yi daidai da 29 ga watan Muharram 1448AH.

Sanarwar ta ce bisa koyarwar Musulunci, Laraba 15 ga Yulin 2026 za ta cika kwanaki 30 na watan Muharram, kafin a fara watan Safar.

Bisa shawarar kwamitin, Sarkin Musulmi ya amince da ayyana ranar Alhamis 16 ga Yulin 2026 a matsayin ranar farko ta watan Safar 1448AH.

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *