Yaran nan da Gwamna Abba ya tsinta suna bacci a bakin titi an nemo iyayen su, yayi musu goma ta arziki

FB IMG 1746390114007

Gwamnan jihar kano, Abba K Yusuf ya hadu da iyayen wayannan yaran a wannan dare a ofishin sa dake fadar Gwamnatin jihar Kano, kamar yadda ya bayar da umarnin a nemo su.

Wayannan yara sune wadanda gwamnan ya gani jiya jiya Asabar akwance akan titi Lodge Road da karfe 2 na dare yayin da ya fita duba aiki a wannan dare.

Gwamnan ya ba da Umarnin a bawa iyayen wayannan yara wadatattun kayan abinci tare da basu kudi domin yin cefane dan ciyar da wayannan yara, inda kuma Gwamnan yai Alkawarin bawa iyayen yaran kudi domin jari suyu Sana’a, kuma dai Gwamnan ya bayar da umarnin Gaggawa domin a sa yaran a makaranta mai kyau tare da dukkan kannansu da suke gida basa zuwa makaranata.

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news ku shiga nan  πŸ‘‡

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group πŸ‘‡πŸ‘‡

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *