Kwanaki biyu bayan yanke hukuncin zaben jihar Kano, Kotun Koli ta sanya ranar raba gardama a shari’ar zaben Kaduna Kotun ta sanya ranar Alhamis 19 ga watan Janairu a matsayin ranar yanke hukuncin karshe kan takaddamar zaben Wannan na zuwa ne bayan Gwamna Uba Sani ya yi nasara a Kotun Daukaka Kara a matsayin halastaccen zababben gwamna a jihar
Alfijir labarai ta rawaito Kotun ta sanar da ranar Alhamis 19 ga watan Janairu a matsayin ranar yanke hukuncin da ake yi a jihar kan zaben gwamna. Kotun Koli za ta yanke hukunci a shari’ar Kaduna ranar Alhamis.
Isah Ashiru Kudan wanda ya yi takara a jami’yyar PDP shi ke kalubalantar zaben Gwamna Uba Sani na jam’iyyar APC a jihar.
A kwanakin baya, Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da nasarar Gwamna Uba Sani a matsayin halastaccen zababben gwamna a jihar. Har ila yau, ta yi fatali da korafe-korafen dan takarar jam’iyyar PDP, Ashiru Kudan saboda rashin gamsassun hujjoji a shari’ar.
Wannan na zuwa ne kwanaki biyu kacal bayan yanke hukuncin zaben gwamnan Kano da ta dauke hankulan mutane a Najeriya baki daya.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/IUuk7jeH4yvAkwOmbOCSfl
