Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya aike da sakon jajantawa Yan kasuwar waya ta Firm Centre dake Kano.
Alhaji Aminu Ado Bayero cikin alhini ya bayyana damuwarsa bisa yadda aka samu asrar dukiyoyi a lokacin tashin gobarar.
Ya bayyana tashin gobarar da cewa wani if’tila’i ne daga ubangiji inda yayi addu’ar Allah ya mayar musu da mafificin abunda suka rasa.
Sarkin Kano Alhaji Aminu Bayero ya bukaci mahukunta dasu duba al’amarin tareda tallafawa Yan kasuwar da suka gamu da wannan if’tila’in.
Kazalika sarkin ya bukaci da aduba tare binciken abubuwan da suke haifar da irin wannan gobara lokaci zuwa lokaci domin maganin al’amurin.
Sa hannu.
Abubakar Balarabe Kofar Naisa Sakataren Yada labarai na Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero CFR, JP, CNOL
9/7/2025
Ga Masu Son Bada Talla A Kira +2348032077835
Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news ku shiga nan 👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇
https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zN