Bayan daddagewa ya yiwa yar matarsa fyaɗe kotu ta yanke masa ɗaurin rai-da-rai

IMG 20240111 234351

Kotu ta yanke wa wani magidanci mai shekara 56 hukuncin ɗaurin rai-da-rai kan laifin yin fyaɗe ga yar matarsa wato agolarsa ’yar shekara 14.

Babbar Kotun Jihar Ekiti ta yanke wa mutumin hukuncin ne bayan an gurfanar da shi kan zargin aikata laifin a watan Oktoban shekarar 2024, watanni bakwai da suka gabata.

A yayin zaman kotun da ke zamanta a garin Ado-Ekiti, mai gabatar da ƙara, Julius Ajibare ya gabatar da shaidu shida da ke tabbatar da laifin da ake tuhumar mijin mahaifiyar yarinyar da yi mata fyaɗe.

Kazalika ya gabatar da wasu hujjoji da kuma sakamakon gwajin asibiti da suka tabbatar da laifin da ake zargin magidancin da aikatawa.

Bisa haka ne kotun ta yanke wa mutumin hukuncin ɗaurin rai-da-rai, bayan ta saurari jawabansa ta bakin lauyansa, Olajide Adedeji, wanda ya gabatar da shaida guda ɗaya.

Aminiya

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news ku shiga nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *