Ana Zargin Gwamnatin Tinubu Da Naɗa Membobin Jam’iyyar APC A Matsayin Kwamishinonin Zaɓe.

IMG 20250609 WA0173

Daga Aminu Bala Madobi

Kungiyar kare haƙƙin ɗan Adam da ɗorewar tattalin arziki, wato SERAP, ta zargi gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da naɗa wasu mambobin jam’iyyar APC a matsayin kwamishinonin zaɓe (RECs) a hukumar INEC, da zummar taimaka masa cin zaɓe a shekarar 2027.

SERAP ta bukaci Shugaba Tinubu da ya soke nadin, inda ta ce hakan zai iya lalata amincewar al’umma da tsarin zabe a Najeriya. A cewarta, a kalla mutum uku daga cikin waɗanda aka naɗa ana zarginsu da kasancewa ‘yan jam’iyya ko kuma na kusa da jam’iyyar APC.

Wasu daga cikin waɗanda aka ambata a matsayin masu alaƙa da APC sun haɗa da:

Etekamba Umoren (Daga Akwa Ibom)

Isah Shaka Ehimeakne (Edo)

Bunmi Omoseyindemi (Lagos)

Anugbum Onuoha (Rivers)

Kungiyar ta ce, “Yin hakan barazana ce ga sahihancin zaɓuɓɓuka da kuma dimokuraɗiyya a ƙasar.”

Har ila yau, SERAP ta bukaci Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi, da ya gabatar da kudiri a gaban majalisa domin karfafa ikon INEC da tabbatar da cewa naɗe-naɗen hukumar basa karkata ga kowace jam’iyya.

A hannu guda, jam’iyyar APC ta bayyana goyon bayanta ga Shugaba Tinubu a zaɓen 2027, tana mai cewa duk da ƙalubalen tattalin arziki, ya nuna bajinta a wasu fannoni.

Ga Masu Son Bada Talla A Kira   +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news ku shiga nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zN

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *