Daga Aminu Bala Madobi
Akalla mutane 25 ne suka mutu a wasu hadurran kwale-kwale a jihohin Jigawa da Bayelsa.
Rahotanni daga karamar hukumar Taura ta jihar Jigawa na cewa, a jiya wani jirgin ruwa dauke da fasinjoji dake tsallaka kogin Gamoda a kauyen Nahuce ya kife, inda mutane 5 suka mutu, wasu 15 kuma suka bace
Kazalika akalla mutane 20 ne suka mutu bayan da wani kwale-kwalen katako ya kama da wuta bayan ya yi bindiga a wani kogi a jihar Bayelsa da ke gabar tekun Najeriya a ranar Laraba, in ji kakakin ‘yan sandan.
Kwale-kwalen dai na dauke da ‘yan kasuwa ne da ke kai kayayyaki zuwa yankunan bakin teku, kamar yadda kakakin rundunar ‘yan sandan Bayelsa Musa Muhammed ya bayyana a ranar Alhamis.
‘Yan kasuwa kan yi tafiye-tafiye na mako-mako tsakanin matsugunan bakin teku da Yenagoa babban birnin jihar.
Akalla dai mutane 200 ne aka rawaito sun rasa rayukansu a hatsarin kwale-kwale a Najeriyar a bara, inda hukumomi kan dora alhakin hakan akan cunkusa mutane da rashin kula da matakan kare aukwar hadurra.Reuters
Sharhi TV
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj