Ƙasar Rasha Ta Magantu Kan Ɗaga Tutarta Da Ake Yi A Zanga-zangar Ƴan Nijeriya

FB IMG 1722881837102

Ofishin jakadancin ƙasar Russia a Najeriya ya musanta hannu a cikin amfani da tutar kasar da wasu masu zanga-zanga ke yi.

Alfijir labarai ta ruwaito qasu masu zanga-zanga na daga tutar ƙasar Russia a yayin zanga zangar a kwanakin nan a jihar da sauran wasu jihohin.

Dama can an zargi ƙasar Rashan da hannu dumu-dumi a rikicin siyasa da ya shafi kasashen Mali da Nijar da Burkina Faso.

Wanda hakan ya haifar da damuwa kan shigar wata kasa daga ketare kan al’amuran da suka shafi cikin gida.

Sai dai a sanarwar da ofishin jakadancin Russia a Najeriya ya fitar ya ce kasar bata shiga al’amuran da suka shafi wata kasa ciki har da Najeriya ba, kuma abinda masu zanga zangar suke yi ya saba da manufofin Russia.

Sanarwar ta kuma ce ƙasar Russia na girmama dimukordiyyar Najeriya.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *