Ngelale ya ce bisa ga umarnin na Shugaban Kasa, nadin ya fara aiki nan take.
Alfijir Labarai ta rawaito Shugaban Kasa Bola Tinubu ya nada Zacch Adedeji a matsayin sabon Shugaban Hukumar Tattara Haraji ta Kasa (FIRS), inda ya sauke mai ci, Mohammed Nami.

Mai magana da yawun shugaban, Ajuri Ngelele ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da yammacin Alhamis.
Ya ce tuni Tinubu ya umarci Nami ya tafi hutun ajiye aiki na tsawon wata uku, kamar yadda dokar aikin gwamnati ta tanada a shirye-shiryen yin ritayarsa ranar 8 ga watan Disamba mai zuwa.
Ngelale ya ce bisa ga umarnin na Shugaban Kasa, nadin ya fara aiki nan take.
“Hon. Zacch Adedeji zai karbi ragamar shugabancin hukumar na tsawon kwana 90 a matsayin rikon-kwarya, kafin daga bisani a tabbatar da shi a matsayin cikakken shugaban Hukumar Tattara Haraji ta Kasa (FIRS), na tsawon shekaru hudu.
“Hon. Zacch Adedeji Akanta ne da ya yi karatu a Jami’ar Obafemi Awolowo, inda ya kammala da digiri mai daraja ta daya. Ba da jimawa ba ya rike muƙamin mai ba shugaban kasa shawara kan tattara haraji, bayan ya yi Kwamishinan Kudi a Jihar Oyo,” in ji sanarwar.
Aminiya
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@musa_bestseller
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/FNim39ly65N2CzcTt8FgWb