Tinubu ya nada shugaban ma’aikata na Lagos da Alh Tanko Yakasai da wasu 14 mukamai

Rahotanni sun bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada shugaban ma’aikata na Legas, Hakeem Muri-Okunola a matsayin babban sakatare.

Alfijir Labarai ta rawaito jaridar Intelregion ta wallafa shugaba ya naɗa Muri-Okunola wanda har yanzu ba a bayyana shi a hukumance ba, an yi shi ne tare da wasu mutane 15 da aka nada da suka hada da:-

Alh Tanko Yakasai,

Adejoke Orelope-Adefulire,

Moremi Ojudu.

Muri-Okunola lauya ne mai shekaru 51, wanda ya shiga aikin a  ma’aikatan Legas a shekarar 2001 a matsayin mataimaki na musamman ga Gwamna Tinubu a lokacin.

Daga baya ya yi aiki a matsayin Babban Sakatare na Kwamitin Amfani da Filaye a 2005.

Bayan shekaru shida, an kara masa girma zuwa sakatare na dindindin kuma aka nada shi shugaban ma’aikata a watan Disamba na 2018.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai  👇

https://chat.whatsapp.com/FNim39ly65N2CzcTt8FgWb

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *