Daga Baba Usman Gama
‘Yan bindiga sun bukaci karin babura guda biyu bayan karbar kudin fansa har naira miliyan 10 bayan sun sace mutane 23 a kauyen Kudiri da ke karamar hukumar Kagarko a jihar Kaduna.
Masu zanga-zanga sun ce zaman Wike a kujerar Minista zai kawowa Bola Tinubu matsala a gwamnati.
Mukaddashiyar Kwamandan Hukumar EFCC ta Kaduna Aisha Abubakar ta jagoranci tattakin Ranar Yaki da Rashawa ta Duniya a jihar.
Gamayyar lauyoyin arewacin Najeriya na shirin maka gwamnatin tarayya a gaban kotu kan harin Kaduna.
An yi wa tsohon shugaban kasar Sierra Leone Koroma daurin-talala.
Mayakan Houthi sun sha alwashin hana jiragen ruwan daukar kaya shiga Isra’ila
Gwamnatin Ghana na shirin karkatar da akalar bautar kasa zuwa bada horo kan aikin gona.
Shugaban Falasɗinawa Abbas ya ɗora alhakin ‘kisan yaran Gaza’ a kan Amurka.
Al’ummar Masar zasu kada kuri’a a babban zaben kasar yau Lahadi.
Ɗan wasan Manchester City Kalvin Phillips, na cikin ƴan wasan farko da Manchester United za ta yi cefane.
EPL: Aston Villa ta sami nasara akan Arsenal da ci 1:0 a wasan jiya.
Laliga: Real Soceidad ta sami nasara akan Villarreal da ci 3:0 a wasan jiya.
Seria A: Atalanta ta sami nasara akan Ac Milan da ci 3:2 a wasan jiya.
Seria A: Inter Milan ta sami nasara akan Udinese da ci 4:0 a wasan jiya.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H47OrRBUPHYEeNqV0vwlQp