Shugaba Tinubu ya cire Abuja daga tsarin Asusun Ajiya na Bai-ɗaya

FB IMG 1696883339680

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya cire birnin tarayyar ƙasar Abuja daga tsarin Asusun Ajiya na Bai-ɗaya (TSA)

Alfijir Labarai ta rawaito an ɗauki matakin ne da nufin bayar da dama wajen bunƙasa ci gaban birnin ƙarƙashin jagorancin ministan Abuja Nyesom Wike, domin ba shi ƙarin iko kan kuɗaɗen da birnin ke tarawa.

Ministan Abuja, Nyesom Wike ne ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi a taron manema labarai da ya gudanar ranar Juma’a a Abuja.

Asusun Ajiya na Bai-ɗaya (TSA) Tsari ne da gwamnatin tarayya ta ɓullo da shi a 2015, da nufin sanya duka kuɗaɗen shiga da gwamnati ke samu a cikinsa, domin tabbatar da gaskiya da bin diddigin kuɗaɗen gwamnati.

BBC

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/K8z1chFesJeCf99QehWJPo

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *