Rundunar ‘yan sandan jihar Sokoto ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da hannu a harin kasuwar kauyen Sokoto da ya yi sanadin mutuwar mutane shida a wani kauye da ake kira Kiri da ke karamar hukumar Gada a jihar Sokoto.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Sokoto, ASP Ahmad Rufa’i ne ya bayyana haka ga wakilin Radio Nigeria Kaduna a wata tattaunawa ta wayar tarho. PPRO na rundunar ‘yan sandan jihar ASP Ahmad Rufa, ya ce an kama wadanda ake zargin dauke da shanu 3 da wata bindiga kirar gida.
A cewarsa, wadanda ake zargin ‘yan asalin Sabon garin Dole ne a karamar hukumar Goronyo a jihar Sokoto kuma duk sun amsa laifin da suka aikata.
A wani labarin kuma, rundunar ‘yan sandan ta ce tana gudanar da bincike kan zargin kashe wani da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da wasu ’yan daba suka kashe a tsohon filin jirgin sama na jihar Sakoto.
Wasu majiyoyi a yankin sun ce wani harin da aka kai ya kai ga halaka wani da ake zargin dan fashi da makami ne.
Majiyar wadda ba ta son a bayyana sunansa ta ce ‘yan sandan sun fara kame wadanda ake zargi da hannu a ciki da suka kashe wanda ake zargin dan fashi da makami ne.
Kakakin ‘yan sandan ya ce shugabannin al’ummar yankin sun tattauna da hukumar ‘yan sanda kuma ‘yan sandan za su dauki matakin da ya dace bayan kammala bincike kan lamarin.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/CJ2q8cmhhOxFY6OEgwV5vk