Jamhuriyar Nijar Ta Fara Ɗaukar Sojojin Sa Kai Don Shirin Yaki

Mayaƙan sa-kan za su taimaka wa sojojin Nijar a filin daga, kula da lafiya da sufuri da sauransu, idan buƙatar hakan ta taso.

Alfijir Labarai ta rawaito Gwamantin sojin Nijar ta fara ɗaukar mayakan sa-kai a shirinta na tunkarar dakarun kungiyar ECOWAS da ke shirin daukar matakin soji da nufin dawo da mulkin dimokuraɗiyya a ƙasar.

Matasa masu akalla shekaru 18 ne za a dauka a rundunar sa-kan mai suna VDN a taƙaice, inda ake tantance su a Filin Wasa na Janar Seyni Kountche da ke birnin Yamai da kuma iyakar ƙasar da Najeriya da Jamhuriyar Benin.

Mayaƙan sa-kan za su taimaka wa sojojin Nijar a filin daga, kula da lafiya da sufuri da sauransu, idan buƙatar hakan ta taso.

Burkina Faso tana rundunar sa-kai mai irin wannan suna, da ta kafa domin taimaka mata yaƙi da ta’ddancin da ke ci wa ƙasar tuwo a ƙwarya.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook.   Alfijir Labarai
YouTube.     Best Seller Channel
Twitter.        @Musabestseller
Instagram.  @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai  👇

https://chat.whatsapp.com/Jmw5CBsPV6H3DbSgnlFUHM

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *