Gwamnatin Tarayya Ta Kara Farashin Mitar Wutar Lantarki A Najeriya

Hukumar da ke kula da wutar lantarki ta Nijeriya (NERC) ta amince da karin farashin mitar wutar lantarki da ake biya a kasar.

 Alfijir Labarai ta rawaito wata takardar da shugabannin NERC, Sanusi Garba da Dafe Akpeneye suka sanyawa hannu kuma mai kwanan wata 5 ga watan Satumba, 2023, ta bayyana cewa, mita mai layi daya za a biya Naira N81,975.16 maimakon Naira N58,661.69 da ake biya a baya, sai kuma mita mai layi Uku, za a biya Naira N143,836.10 maimakon Naira N109,684.10

Takardar ta ce, an sabunta farashin ne don tabbatar da daidaiton farashin mitoci ga masu amfani da wutar.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

7 https://www.threads.net/@musa_bestseller

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai  👇

https://chat.whatsapp.com/FNim39ly65N2CzcTt8FgWb

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *