
Alfijr ta rawaito Gwamnan Jihar Kano Engr Abba Kabir Yusuf ya amince da karin Naɗin mukamai biyar.
Sakataren yada labaran gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar da sanarwar tare da sanyawa hannu, kamar haka.
1. Injiniya Garba Ahmed Bichi
Manajan Daraktan Hukumar Ruwa ta Jihar Kano
2. Dr. Rahila Mukhtar
Babban Sakataren Hukumar Kula da Gudunmawar Kiwon Lafiya ta Jihar Kano (KCHMA).
3. Hassan Baba Danbaffa
Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tituna ta Jihar Kano (KARMA).
4. Arc. Ibrahim Yakubu
Manajan Daraktan hukumar tsara Birane ta Jihar Kano (KNUPDA).
5. Abdulkadir Abdussalam
Akanta Janar na Jihar Kano
Ya kara da cewa nan ba da jimawa ba za a sanar da bikin rantsar da wadanda aka nada domin ba su damar sauke nauyin da aka dora musu nan take.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Alfijr Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/GdLiqZyHuSz5NhjdGoGRGZ
Allah yay riqo da hannayensu, yayi musu jagoranci.