Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya tsallake rijiya da baya a wani yunkurin kashe shi da wasu ‘yan bindiga sanye da kayan sojoji suka yi a hanyar Lokoja zuwa Abuja.
Alfijir labarai ta rawaito lamarin ya zo a lokacin zaben gwamnan jihar da za a yi a ranar 11 ga watan Nuwamba cewar kwamishinan yada labarai da sadarwa na jihar Kingsley Femi Fanwo.
Ya ce an yi yunkurin kashe Gwamna Bello ne a tazarar kilomita kadan daga Abuja
An ce gwamnan yana kan hanyarsa ta zuwa wani aiki ne a Abuja daga Lokoka, babban birnin jihar Kogi, aka yi yunkurin kashe shi.
“Harin ya faru ne da misalin karfe 4 na yammacin ranar Lahadi, 22 ga Oktoba, 2023.
“Maharan da ke sanye da kakin soji sun tare ayarin motocin Gwamnan suka yi ta harbe-harbe a kan motarsa da sauran motocin da ke cikin ayarin.
Sai da jami’an tsaro da ke tare da Gwamnan suka shiga cikin gaggawa domin dakile shirin sojojin da ba a san ko su waye ba.
“Hare-haren sun kasance a wurare uku daban-daban, shingen karshe ya kasance a kusa da babban birnin tarayya Kwali da misalin karfe 4:20 na yamma.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/K8z1chFesJeCf99QehWJPo