Gwamnan Jihar Katsina, Dakta Dikko Umar Raɗɗa, ya naɗa matashiya mai shekaru 25 ƴar asalin jihar Katsina, mai suna Rabi’atu Sulaiman, a matsayin mai taimaka masa kan sabbin kafafen sada zumunta (Special Assistant on Digital Media) a gwamnatinsa.
Alfijir Labarai ta rawaito matashiyar wadda Gwamna Raɗɗa, ya naɗa tana daga cikin jarumai mata da ake gudanar da shirin Film ɗin “Ƙwana Casa’in, da ita mai dogon zango da ake haskawa a tashar Arewa 24, wacce aka fi sani da suna Khairiyya.
Haka kuma babu dadewa aka zabeta a cikin shirin manyan mata domin taka rawa a shirin.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Alfijir Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/Jmw5CBsPV6H3DbSgnlFUHM