EFCC Ta Kama Wadansu Da Maƙudan Kudaden Siyan Kuri’u A Kano Da Katsina

Alfijr ta rawaito Hukumar Yaki da Yiwa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta ce ta kama wasu mutane 12 da ake zargi da sayan kuri’u a karin zaben da aka yi ranar Asabar a jihohin Kano da Katsina.

Kwamandan EFCC na shiyyar Kano, Faruk Dogondaji, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN, a wata hira da ya yi da manema labarai cewa, an kama wadanda ake zargin da tsabar kudi Naira miliyan 1.5 a jihohin Kano da Katsina.

A cewarsa, an kama mutane 10 ne a karamar hukumar Doguwa ta jihar Kano, biyu kuma a karamar hukumar Kankia ta jihar Katsina.

Dogondaji ya ce an kama wadanda ake zargin ne a lokacin da suke kokarin jawo masu kada kuri’a da kudade a wasu rumfunan zabe.

Ya ce an kama wadanda ake zargin su 10 ne da Naira miliyan 1,357,500 a karamar hukumar Doguwa, yayin da aka kama mutanen biyu da N242,000 a karamar hukumar Kankia.

“Har ila yau, za mu kasance a jiki a duk cibiyoyin tattarawa don hana canjin sakamako,” in ji shi.

Ya ce kasancewar jami’an da ke gudanar da zaben zai kara sahihanci ga aikin.

Kwamandan na EFCC ya ce za a gurfanar da wadanda ake zargin a kotu bayan bincike.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Alfijr Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/G1wNveF9mGU7jec5mWhFvZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *