Da Ɗumi Ɗuminsa: Obi Ya Kayar Da Atiku, Tinubu A Cikin Fadar Shugaban Kasa

Alfijr ta rawaito Dan Takarar Shugaban Kasa na Jam’iyyar Labour, ya yi nasara a daya daga cikin rumfunan zabe da ke cikin fadar Shugaban kasa a Abuja.

A PU 131 da ke gaban Pilot Gate a fadar gwamnatin tarayya Abuja, Obi ya samu kuri’u 17 yayin da Asiwaju Bola Tinubu na jam’iyyar APC mai mulki ya samu kuri’u 6, sannan tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP. ) ya samu kuri’u 3.

Jam’iyyar Obi ta kuma lashe zaben ‘yan majalisar dokokin kasar a rumfunan zabe.

Ga sakamakon:

SANATA APC – 5 PDP – 3 APGA – 1 NNPP – 1 LP – 13

Marasa inganci – Babu Total = 23 Majalisar Wakilai PDP – 1 APC – 5 Labour Party – 15 ADC – 1 Invalid – 1 Total = 23

Daily Trust

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Alfijr Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/KrigvNKcneVBHxctLUQ0ux

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *