Babbar Kotun Tarayya ta kori karar da APC ta shigar kan hana biyan kuɗaɗen kananan hukumomin jihar Kano

FB IMG 1753107424455

Babbar Kotun Tarayya mai lamba 3 da ke Kano ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Simon Amobeda ta kori karar da jam’iyyar APC tare da Hon. Abdullahi Abbas da Hon. Aminu Aliyu Tiga suka shigar domin hana biyan kuɗaɗen kananan hukumomi a jihar Kano.

Masu ƙarar sun nemi kotun ta dakatar da biyan kuɗaɗen kananan hukumomi bisa hujjar cewa an karya umarnin kotu da ya hana gudanar da zaɓen kananan hukumomi a jihar.

A yayin zaman kotun, lauyan masu ƙara ya roƙi kotun da ta jingine sauraron shari’ar, amma lauyan gwamnatin Kano ya bukaci kotun ta kori karar gaba ɗaya tare da biyan diyya.

A ƙarshe, Mai Shari’a Amobeda ya yanke hukunci inda ya kori karar baki ɗaya.

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *