Ambaliyar ruwa  mai tsananin karfi ta hallaka mutane da dama tare da lalata gidaje da  kadarori a Neja

FB IMG 1748551679720

Rahotanni daga Karamar Hukumar Mokwa ta Jihar Neja, sun bayyana cewa ambaliyar ruwa  mai tsananin karfi ta hallaka mutane da dama tare da lalata gidaje da  kadarori na miliyoyin nairori.

Mazauna garin sun ce  sakamakon ambaliyar ruwan, hanyar da ke hada shiyyar Arewa da  Kudancin Najeriya ta karye.

To sai dai  har zuwa yanzu ba a tabbatar da cikakken adadin wadanda suka mutu ba.

Wasu daga cikin mazauna yankin sun bayyana cewa akalla mutane 50  ake zargin sun mutu wadanda yawancinsu  mata ne da kananan yara, yayinda har zuwa Lokacin hada wannan rahoto ba akai da gano wasu daga cikin wadanda ruwa ya yi gaba da su ba.

Ambaliyar dai  ta faru ne sakamakon ruwan sama mai karfi da aka yi a daren Laraba da ya dauki tsawon lokaci ya na zuba.

Rahotanni sun nuna cewe yadda alummar yankin  ke rokon hukumomi da su kai musu daukin  gaggawa.

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news ku shiga nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *