Martanin Kwamishina Waiya Ga AVM Ibrahim Umar Kan Zargin Gwamnatin Kano Da Badakala

IMG 120335 21626 1782039829007

Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida, Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya, ya kalubalanci AVM Ibrahim Umar (ritaya), tsohon Kwamishinan Harkokin Tsaro na Cikin Gida da Harkokin Musamman, da ya fito ya bayyana irin badakalar da ya zargi Gwamnatin Kano da aikatawa cikin awa 24.

Waiya ya ce idan Umar bai fito ya bayyana hujjojinsa cikin wa’adin da aka ba shi ba, to za su fito da abin da suka kira badakalar da ya aikata ta kuΙ—aΙ—e a hukumar ayyuka na musamman da ke fadar gwamnatin jihar Kano, da kuma ma’aikatar tsaro ta cikin gida da harkoki na musamman, kafin ya bar mukaminsa.

Ya Ζ™ara da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da bin diddigin dukkan zarge-zarge tare da tabbatar da gaskiya a kan duk abin da aka bayyana.

Don haka kwamishina Waiya ya kara da cewar, tsohon kwamishina AVM Ibrahim Umar, mun baka sa’o’i 24 ka fito da badakalar gwamnati da kace, ko mu mu fito da taka.

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan πŸ‘‡

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group πŸ‘‡πŸ‘‡

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *