Gwamnatin Tarayya ta buɗe cibiyar fasahar sadarwa da aka ƙona a lokacin zanga-zanga a Kano

FB IMG 1751562147035

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da cibiyar Fasahar Sadarwa ta Zamani (Digital Industrial Park) a Jihar Kano, wacce aka ƙone ta  yayin zanga-zangar matsin rayuwa a ranar 1 ga watan Agusta 2024.

Ministan Sadarwa da Fasaha, Dr. Bosun Tijani, wanda ya ƙaddamar da cibiyar a madadin shugaban kasa, ya yabawa kamfanin IHS Nigeria saboda gaggauta sake gina cibiyar ba tare da amfani da kudin gwamnati ba.

A cewar Tijani, an kafa cibiyar ne domin baiwa matasa damar koyon fasahar zamani don taimaka wa rayuwarsu.

Ministan ya ce lalata cibiyar, lokacin da ake da da buɗe ta a bara, abun takaici ne, inda ya ƙara da cewa “amma takaicin bai kashe mana gwiwa ba har sai da mu ka sake gina ta.”

A nasa ɓangaren, Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce cibiyar alama ce ta jajircewar jihar wajen tallafa wa matasa da bunkasa tattalin arzikin su.

Gwamnan wanda ya samu wakilcin mataimakinsa , Aminu Abdussalam Gwarzo ya ce tun shigowarsa Gwamnati a 2023, jihar ta mayar da hankali kan shirye-shiryen da zasu tallafawa matasa a fannin sadarwa.

Hukumar NCC, ta bakin shugaban ta na ƙasa, Dr Aminu Mai ta bayyana cewa an kafa irin wannan cibiyar a Borno, Ogun da Enugu domin samar da sabbin masu fasaha a Najeriya.

Maida ya ce irin waɗannan cibiyoyin za su yi amfani wajen bincike da bunkasa ilimin fasaha don bukatar tattalin arzikin ƙasa.

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *