An hana alkalai da lauyoyi shiga kotuna a Abuja yayin da JUSUN ta fara yajin aikin sai baba-ta-gani
Alkalan kotu, lauyoyi, ma’aikatan kotu da masu shigar da kara sun kasa shiga hedikwatar Babbar Kotun Tarayya (FHC) da ke Abuja, bayan da mambobin Kungiyar Ma’aikatan Harkokin Shari’a ta Najeriya (JUSUN) suka fara yajin aikin sai baba-ta-gani daga ranar Litinin.
An rufe dukkan kofofin shiga cikin harabar kotun da ke kan titin Shehu Shagari, lamarin da ya haddasa tsaiko ga duk wani aiki da ya shafi kotun.
Yajin aikin ya shafi wasu manyan kotuna da ke cikin babban birnin tarayya (FCT), ciki har da Kotun Daukaka Kara da ke Abuja da Babbar Kotun Abuja, inda aka rufe su baki daya.
Daily Nigerian
An fara wannan yajin aiki ne bisa umarnin shugabancin kasa na JUSUN, wanda ya umurci dukkan shugabannin reshe na kungiyar da su tabbatar da cewa mambobi sun zauna a gida tun daga tsakar daren ranar 1 ga Yuni.
Ga Masu Son Bada Talla A Kira +2348032077835
Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news ku shiga nan 👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇
https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zN
