Biyo bayan samamen da jami’an tsaro suka kai shelkwatar ƙungiyar kwadago ta ƙasa NLC, kungiyar ta kira taron gaggawa na kwamitin koli a gobe Asabar.
Alfijir labarai ta ruwaito hakan na zuwa ne a yayin da kungiyar marubuta Ƴan kwadago ta LAWAN ta shiga jerin kungiyoyin dake Alla-Wadai da kai samamen.
Idan za a iya tunawa dai, a ranar Laraba ne jami’an tsaro suka yi dirar mikiya a ofishin na NLC dake Abuja.
A cewar ƙungiyar, jami’an tsaron sun tafi da wasu takardu da suke zargin da su aka yi amfani wajen tunzura matasa don su fito zanga-zanga.
Jaridar Vanguard ta wallafa cewa kungiyar ta shirya taron gaggawa a gobe Asabar da misalin karfe 4 domin daukar mataki kan samamen.
Ana saran taron zai gudana ne ta kafar Internet.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj