
Alfijr ta rawaito Wani mutum mai shekara 53 da ke kera laya mai hana harsashi ga ‘yan ta’adda da masu aikata laifuka a jihar Katsina, yanzu haka yana taimakawa ‘yan sanda da karin bayani kan ayyukansa.
SP Gambo Isah, kakakin rundunar na jihar ya tabbatar wa manema labarai cewa wanda ake zargin yana zaune ne a hanyar Maiduguri a karamar hukumar Sabuwa a jihar.
Ya kara da cewa a ranar Asabar, 26 ga watan Nuwamba, 2022, bayan da aka samu labari, ‘yan sanda sun kama wanda ake zargin a Katsina.
Ya kuma bayyana cewa ana siyar da laya mai hana harsashi ga ‘yan ta’adda da sauran masu aikata miyagun laifuka a jihohin Zamfara, Kaduna da Katsina kan Naira 60,000 kan kowacce guda.
Ya kara da cewa an kama wanda ake zargin ne da laya guda hudu da aka lullube a cikin riguna.
Wanda ake zargin, a cewar Isah, ya kuma amsa cewa ya rika gudanar da addu’o’i a kai ga ‘yan bindigar domin samun nasara a gudanar da ayyukansu, na rashin kamawa ko cutar da su daga jami’an tsaro.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Best seller Channel
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/I4L1E0rIZp23nVG7Mtt47c