Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya mika karin sunayen mutanen da yake son nadawa ministoci ga Majalisar Dattawa.
Tinubu ya aike wa majalisar sunayen ne a yayin da take tsaka da tantance karashen mutane 28 da ya aike mata da farko a ranar Laraba.
Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila ya mika sunayen ga Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswil Akpabio.
A makon jiya ne Tinubu ya mika wa majalisar sunayen rukunin farko na mutanen da yake son nadawa ministoci daga 25 daga cikin jihohi 36 da birnin tarayya da ke kasar — saura jihohi 11.
Jihohin da ake jiran sunayensu ne shugaban kasar ya mika sunayen ministocinsu su ne: Kano, Legas, Kebbi, Filato, Adamawa, Zamafara, Gombe, Yobe, Edo, Bayelsa, da kuma Osun.

Mutanen da ya fara bayarwa sun hada da mata bakwai da maza 21, wadanda cikinsu kuma akwai tsoffin gwamnoni hudu; ’yan majalisa masu ci uku, tsoffin ‘yan majalisa uku, hadiman shugaban kasa uku, da shugaban hukumar gwamnati daya.
A jerin sunayen da ya bayar da farko, jihohi biyu, Katsina da Kuros Riba sun samu mutum biyu kowannensu.
Aminiya
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Alfijir Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/BW0j8s7exuQ7ojpyCVMtfI
Âllâh yâkârâ maku daukaka