Alfijr ta rawaito a kalla mutane shida, ciki har da wata mace ‘yar shekara 120 sun mutu, yayin da wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan fashi ne Sanadin a kauyen Raka da ke karamar hukumar Tangaza a jihar Sakkwato.
An kuma ce maharan sun kona gidaje da kayan abinci da dama kafin su tafi da dabbobin gida da ba a bayyana adadinsu ba.
Hakimin gundumar, Alhaji Sa’idu Wakili wanda ya tabbatar da harin da aka kai gidajen da kayan abinci, ya ce babu wani garkuwa da ‘yan bindigar suka yi, amma an kashe wata mata ‘yar shekara 120 tare da wasu biyar.
Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da na jihohi da su kara zage damtse wajen magance matsalolin tsaro a yankin.
Hakimin ya kuma yi kira ga masu hannu da shuni da su samar da gagarumin hanyoyin kare rayuka da dukiyoyin al’ummar yankin.
A nasu bangaren, shugaban riko na karamar hukumar Tangaza Alhaji Ibrahim Lawal Junju da mai ba da shawara na musamman kan harkokin tituna, Engr. Mai Damma Tangaza wanda ya je yankin domin jajantawa wadanda abin ya shafa, ya kuma yi nazarin irin barnar da ‘yan ta’addan suka yi, ya kuma bayyana hare-haren a matsayin abin takaici, ya kuma yi kira ga al’umma da su dauki lamarin a matsayin jarraba ce, ya kuma yi alkawarin mika sakamakon binciken da suka samu ga ‘yan ta’adda, gwamnati don taimakon da ya dace ga wadanda abin ya shafa.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Best seller Channel
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇