Wata Sabuwa! Kamfanin MTN Ya Rufe Ofisoshinsa A Faɗin Najeriya

FB IMG 1722340598755

Kamfanin MTN ya sanar da rufe dukkan ofisoshin sa dake Najeriya daga yau Talata 30 ga watan Yuli.

Wani jami’i a kamfanin ne ya tabbatar da hakan ga jaridar TheCable.

Majiyar ta ce an ɗau matakin ne sakamakon farmakin da fusatattun mutanen da aka rufewa layuka suka kai wa kamfanin.

A ranar 27 ga watan Yuli ne dai ƴan Najeriya da dama suka kai kokensu bayan hana su amsa kira da yin kira a layukan nasu sakamakon rashin tantance lambar NIN dinsu.

A ranar Litinin ne wasu fusatattu masu amfani da layukan suka farmaki ofishin MTN dake Festac a jihar Legas.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *