Majalisar Masarautar Adamawa ta tube rawanin Hakimin Ribadu da ke Karamar Hukumar Fufore a jihar, Alhaji Gidado Abubakar.
Alfijir Labarai ta rawaito muƙaddashin Sakataren masarautar, Alhaji Kabiru Bakari, ne ya sanar da hakan a cikin wata takarda da ya aike wa tubabben hakimin.
“Majalisar Masarautar Adamawa ta umarce ni da in rubuta in kuma sanar da kai cewa Gwamnan Jihar Adamawa ya amince da korar ka.
“Ka mika duk wasu takardun hukuma da ke hannunka, ciki har da takardar shaida, ga Mukaddashin Sakataren Masarautar Adamawa da ke Yola,’’ in ji wasikar.

Aminiya
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H47OrRBUPHYEeNqV0vwlQp