Wasu barayi sun kai farmaki wata makabarta sun kuma sace kofar makabarta a jihar Katsina”
Alfijir labarai ta rawaito wasu jama a da suka je rakiyar Wani bawon Allah da ya rasu sun koka dangane da yadda suka ga yanayin makabartar ke ciki, duba da yadda ciyawa ta mamaye ko ina, a wani bangarenma ba’a ganin kaburburan da suke gurin saboda ciyawa, wasu guraren kuma kaburburan suna bukatar gyara domin tukanen har sun fito wasu ma sun bude.
A tattaunawar wakilinmu da Wani bawon Allah ya ce, ina amfani da wannan damar in yi kira na musamman ga Karamar hukumar Rimi da ma mai girma Kauran Rimi da masu hannu da shuni akan su gaggauta daukar matakin da ya dace akan yanayin da wannan makabarta ke ciki da ma wasu manya ayyukan da suka shafi sadaukarwa.
Katsina City News
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/IUuk7jeH4yvAkwOmbOCSfl