Takaitattun Labaran duniya na Yammacin Laraba 15/11/2023 – 01/05/1445AH

best seller i

Daga Baba Usman Gama

Shugaba Tinubu na shirin ganawa da shugabannin ƙasashen duniya a birnin Bissau na ƙasar Guinea domin halartar bikin cikar kasar shekara 50 da samun ‘yancin kai.

Gwamnatin tarayya ta shiga ganawa da kungiyar kwadago don neman hanyoyin da za a bi don kawo karshen yajin aikin da kungiyoyin suka shiga.

Mai ba wa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro Nuhu Ribadu, ya ba wa Kungiyar Kwadago hakuri tare da neman su janye yajin aikin da suka fara.

Jami’ar Bayero ta Kano ta dakatar da jarabawar zangon farko shekarar 2022/2023 sakamakon yajin aikin da kungiyar kwadago ta fara.

Wata mata mai suna Shamsiyya Yunusa ta nemi Kotun Shari’ar Musulunci da ke zamanta a Filin Hockey a Jihar Kano da ta nema wa danta mahaifi daga cikin maza biyun da ta rabu da su.

Domin Kallon Shirin FATAKE Mai Dogon Zango Season 1 Da Kuma CIgaba Da Kallon Season 2, Danna wannan Link din👇

https://youtube.com/@ukentertainmentkano?si=PPtuxJz76OuNP_oI

Mutum 4 sun mutu wasu sun jikkata a hatsarin mota a jihar Abiya.

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta kammala sauraron shari’ar zaɓen gwamnan Nasarawa.

Majalisar Dattawa ta rantsar da Austin Akobundu na jam’iyyar PDP da ke wakiltar Abia ta Tsakiya a Majalisar bayan yayi nasara a kotu.

Wasu da ake zargin barayi ne a yau sun sace wayar tsohon Ministan Watsa Labarai, Labaran Maku a kotun daukaka kara da ke Abuja.

Shugaba Erdogan na Turkiyya yace kasar sa za ta tabbatar wadanda ke da hannu a kisan kiyashin Gaza sun fuskanci shari’a.

Gwamnatin Ghana ta amince ta karawa ma’aikata albashin da yawansa ya kai kashi 23.

An tsare ‘Yan jaridun Togo biyu saboda zargin minista.

‘Yan majalisar dokokin Uganda sun amince a kawo karshen shigar da mai ta Kenya.

Majalisar Dinkin Duniya za ta koma kai kayan agaji ta sama zuwa Nijar.

Shugaban Sudan ta Kudu ya kori shugaban ‘yan sanda bayan jita-jitar juyin mulki.

Babban jami’in Manchester United, Richard Arnold zai sauka daga muƙaminsa wanda shine ya maye gurbin Ed Woodward a matsayin mai babban muƙamin mahukuntan ƙungiyar a watan Fabrairun 2022.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H47OrRBUPHYEeNqV0vwlQp

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *