Daga Baba Usman Gama
Yau Alhamis Kotun Ƙolin Najeriya za ta yi zama kan shari’ar da Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya daukaka kan taƙaddamar nasarar zaɓensa.
Hukumar Shari’a (NJC) ta kara wa alkalai 11 karin girma zuwa Kotun Koli.
Gwamnatin jihar Kano ta ce sakataren Gwamnatin jihar Dr. Abdullahi Baffa Bichi ya karbi hutu domin ya yi jinya a kasar Saudiya, shugaban ma’aikatan gwamnatin Jihar zai kula da ofishin SSG.
Jami’an rundunar ƴan sandan jihar Ogun sun kama waɗanda ake zargin sun kashe wani ɗalibin jami’ar OAU ɗan 100L, Quadri Salami.
PDP ta umurciyayanta da suka gurfanar da ita a gaban kotu sakamakon rigingimun cikin gida, da su janye kararrakin saboda ta samu bude hanyar sulhu da dai-daita tafiyar jamiyyar daya`yan nata.q
Harin Kaduna: MDD tace dole ne Najeriya ta sake duba dokokin kai hari.
Amurka ta tuhumi sojojin Rasha huɗu da laifukan yaƙi.
Matsalolin tsaro a Jamhuriyar Congo na kara tabarbarewa gabanin zaben kasar.
Al Jazeera ta ce Isra’ila ta kashe dangin wakilinta 22 a Gaza.
An yi jana’izar sojojin da aka kashe a yunkurin juyin mulki a Sierra Leone.
Iran na shirin kaddamar da burin aika mutum sararin samaniya bayan da ta yi nasarar harba roka.
”Yan Nijar” sunce kasashen waje ke amfana da kungiyar G5 Sahel.
EPL: Manchester United ta sami nasara akan Chelsea da ci 2:1 a wasan jiya.
EPL: Aston Villa ta sami nasara akan Manchester City da ci 1:0 a wasan jiya.
EPL: Liverpool ta sami nasara akan Sheff. United da ci 2:0 a wasan jiya.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H47OrRBUPHYEeNqV0vwlQp