Shugaban Karamar Hukumar Lokoja, Hon. Mohammed Dan Asabe Muhammad, ya rasu.
Alfijir Labarai ta rawaito an tabbatar da rasuwarsa da misalin karfe 4:30 na safe a wani asibiti da ke Lokoja babban birnin jihar.
An garzaya da Muhammed asibiti bayan da ya yanke jiki ya faɗi a gidansa.
An ce ya halasci tarurrukan siyasa ne na shirye-shiryen zaben gwamnan da za a yi a gobe Asabar.
Wata majiya daga dangin mamacin ta ce an garzaya da shi asibitin Shifa, Lokoja, jim kadan bayan ya faɗi a gidan da yammacin ranar Alhamis.
“Likitoci sun tabbatar da mutuwarsa a asibiti da misalin karfe 4:30 na safiyar ranar Juma’a,” in ji wani dangin da ya nemi a sakaya sunansa.
Marigayin ya fito ne daga mazabar B dake yankin Lokoja.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H47OrRBUPHYEeNqV0vwlQp
IBRAHIM IDRIS MUHAMMAD