Shugaba Buhari Zai Karɓi Lambar Yabo Daga ECOWAS Kan Kare Dimokraɗiyya

Alfijr ta rawaito Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai karbi lambar yabo daga kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS, bisa nasarorin da ya samu a fannin tsaro da inganta dimokuradiyya a yankin.

Garba Shehu, mai magana da yawun shugaban kasar ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata cewa, Umaro Sissoco Embalo, shugaban kungiyar ECOWAS ne ya sanar da hakan a ganawar da suka yi da Buhari a gefen taron majalisar dinkin duniya karo na 5 kan kasashe mafi karancin ci gaba a Qatar.

Ana sa ran Buhari zai dawo kasar a ranar Laraba 8 ga Maris, 2023.

Shehu ya ruwaito Embalo na cewa shugaban Najeriya ya yi fiye da kowa wajen goyon bayan gwamnatocin dimokaradiyya a Afirka ta Yamma kamar yadda ya yi nasa na musamman a yakin da ake yi da ‘yan tawaye, bullar gwamnatocin da ba na demokradiyya ba.

Shugaban ECOWAS ya ce Buhari zai sanya sunansa a cikin “Roll of Honour” a sabon ginin hedikwatar al’umma bayan an kammala shi a Abuja.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook.   Alfijr Labarai
YouTube.     Best Seller Channel
Twitter.        @Musabestseller
Instagram.  @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 

https://chat.whatsapp.com/G1wNveF9mGU7jec5mWhFvZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *