Ma’aikata sun kulle Gwamna Cikin Sakatariyar jihar Kan Kudadensu

Daga Aminu Bala Madobi

Ma’aikatan gwamnatin jihar Oyo sun kulle kofar shiga sakatariyar jihar, inda suka dage da yin magana da gwamna Seyi Makinde kan batutuwa da dama da suka shafi muradun jihar.

Alfijir Labarai ta rawaito ɗaya daga cikin batutuwan a cewarsu, shi ne yadda ake cire masu albashi ba bisa ka’ida ba.

Wani kuma shi ne gazawar gwamna wajen samar da kayan agaji ga ma’aikata.

Wadanda suka halarci zanga-zangar sun hada da ma’aikata da ‘yan fansho daga kungiyar kwadago ta Najeriya NLC, TUC, kungiyar ‘yan fansho ta Najeriya (NUP), kungiyar ma’aikatan kananan hukumomin Najeriya (NULGE) da sauran kungiyoyi.

Shugabannin kungiyarsu da ma’aikatansu suma suna neman a biya su alawus-alawus na hutu ga wadanda suka yi ritaya wadanda suka tsaya cak tun shekarar 2021 da kuma fitar da wasikun karin girma na shekaru 2021 da 2022.

Babu wani jami’in gwamnati da ya yi jawabi ga ma’aikatan da suka yi zanga-zangar a lokacin ba da wannan rahoto.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Alfijir Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *