Kotu Tayi Watsi Da Ƙarar Ɗan Takarar Majalisar Jiha Na Apc Kan Dan Majalisar NNPP A Bebeji

Daga Nazifi Kwankwaso

Kotun sauraren korafin zabe dake nan kano tayi watsi da karar da Dan takarar majalisar jiha na jamiyyar APC a karamar hukumar bebeji Hon Auwal Ibrahim ya shigar gabanta Yana kalubalantar sahihancin Dan takarar majalisar jiha na jamiyyar NNPP hon Ali Mahd Tiga.

Alfijir Labarai ta rawaito Hon Auwal Ibrahim na jamiyyar APC yace Wanda yayi Kara ba Dan jamiyyar NNPP bane, Kuma yayin zabe an Sami aringizon kuri’u Wanda hakan ya sanya hukumar zabe ta inec ta bayyana shi a matsayin wanda yayi Nasara.

Da yake hukunci Mai sharia L B Owolaba yace Mai Kara ya gaza gabatar da kwararon hujoji da zasu gamsar da kotun, don haka kotun tayi watsi da karar nan take.

Lauyan jamiyyar NNPP Barista Bashir Yusif Muhd Tudun Wuzurchi yace, wajibi ne su godewa Allah bisa wanan Nasara, ya Kara da cewa zuwa yanzu jammiyarsu ta NNPP tayi Nasara a ƙararrakin zaɓe 13 da aka shigar dasu a kotunan sauraren korafin zabe.

Lauyan dake kare Hon Auwal ya aka tuntubebshi yaki cewa komai akan batun

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@musa_bestseller

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/FNim39ly65N2CzcTt8FgWb

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *