Gabora ta tashi a wani bangare na hukumar shari’a ta jihar kano a yau Talata, lamarin da ya janyo asarar dukiya mai tarin yawa a ofisoshin dake bangaren.
Alfijir Labarai ta rawaito Hajiya Batulu Isah Waziri babbar daractan kudi da mulki ta tabbatar da faruwar lamarin, Inda ta ce wutar ta faraci misalin karfe 01:30 dai dai lokacin da aka shiga sallar azuhur.
Ta ce wutar ta kone ofisoshin da ke ɓangaren, amma ba a samu asarar rai ba, sai dai ta dukiya.
Jami’an kashe gobara sun sami nasar kashe gobarar bayan da jami’an mu suka sanar da su faruwar lamarin. In Ji Batulu
Hukumar shariah dai itace hukumar da ke kula da abin da ya shafi harkokin addini, masallatai
da makarantun addini da abinda ya shafi lokutan sallah da Nisabin zakka da sauransu.


Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H47OrRBUPHYEeNqV0vwlQp