An tura injinan kashe gobara wurin da lamarin ya faru, sai dai da alama suna fuskantar kalubale wajen kashe gobarar
Wata mummunar gobara ta tashi a wani ginin ‘yan sanda da ke Ismailia na gabar Mashigin Suez da ke Masar ranar Litinin, a cewar ganau da kafafen watsa labarai na kasar.
Wasu bidiyoyi da aka rika wallafawa a soshiyal midiya sun nuna yadda hayaki mai kauri yake tashi a ma’aikatar tsaro ta birnin, kuma da alama babbar kofar shiga ma’aikatar ta fadi.
Ganau guda biyu sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa an tura injinan kashe gobara wurin da lamarin ya faru, sai dai da alama suna fuskantar kalubale wajen kashe gobarar.
Kawo yanzu ba a sani ba ko gobarar ta yi sanadin mutuwa ko jikkatar mutane.
Majiyoyi a hukumomin tsaro na farin-kaya sun ce wasu bangarori na ginin sun fadi sakamakon gobarar.
Reuters
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/FNim39ly65N2CzcTt8FgWb