Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da mutuwar wani yaro mai kimanin shekaru hudu mai suna Abubakar Sani sakamakon gobarar da ta tashi a Yakasai Layin Inuwa mai mai karamar hukumar birnin kano .
Alfijir labarai ta rawaito Jami’in hulda da jama’a na hukumar, Alhaji Saminu Abdullahi ya bayyana hakan a Kano.
Saminu ya bayyana cewa, hukumar ta samu kiran gaggawa daga ma’aikacinsu Habibi Adamu game da barkewar gobara a Yakasai.
Ya kuma yi nuni da cewa, nan take aka hada tawagar ceto daga Ofishin hukumar kashe gobara dake Sakatariyar Audu Bako a birnin Kano .
Jami’in hulda da jama’a ya yi nuni da cewa, ginin bene daya mai tsawon mita 40 da 30 da ake amfani da shi a matsayin gidan zama, daki daya dake benen ne ya kone gaba daya sakamakon gobarar, yayin da falo daya ya dan kone.
Ya ce, Yaron ya makale a dakin da wuta ta kama har ta cinye shi kuma duk kokarin da aka yi na ceto shi kafin isowar ‘yan kwana-kwana ya ci tura.
Saminu ya ci gaba da cewa, an ceto wanda abin ya shafa a sume kuma aka kai shi asibitin kwararru na Murtala Muhammed, inda likitan da ke bakin aiki ya tabbatar da rasuwarsa.
Jami’in hulda da jama’a ya bayyana cewa, an mika mamacin ga mahaifinsa, Sani Hussaini domin yi masa jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
Ya ce gobarar ta tashi ne sakamakon yadda yaron da abin ya shafa ke wasa da ashana a cikin daki.
Saminu ya bukaci iyaye da su daina jefa ’ya’yansu cikin hadari ta hanyar barin su ba tare da kula da su ba da kuma nisantasu da abubuwa masu hadari .
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H3iC9eVfJI012LJzvCQn5V