Ibtila’i: Sarki Sanusi ya baiwa ƴan kasuwar ‘Farm Centre’ tallafin Naira miliyan 10

FB IMG 1749307566148

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi ll ya baiwa ƴan kasuwar waya ta Farm Centre tallafin Naira miliyan 10 sakamakon gobara da ta ƙone shaguna da rumfuna 47 a kasuwar a jiya Juma’a.

Sarkin ya bayyana wannan tallafi ne yayin da ya kai ziyarar nake ga kasuwar, inda ya shawarci su buɗe asusun tallafi don farfaɗo da sashen da ya kone a kasuwar, lamarin da ya haifar da nasara dukiya ta miliyoyin Naira.

A cewar Sarki Sanusi, ya bada tallafin kuma ya na kira ga waɗanda abun ya shafa da su buɗe asusun tallafi su kuma aikewa duk wanda ya ke kasuwar.

Ya kara da cewa nan gaba kadan za a tara makudan kudade da za su isa a gyara kasuwar, su kuma yan kasuwa su rage asara.

Sarki Sanusi ya kuma yi addu’ar Allah Ya kiyaye faruwar gobarar nan gaba, inda ya yi wa wadanda lamarin ya shafa addu’ar Allah Ya kawo musu ɗauki.

Ga Masu Son Bada Talla A Kira   +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news ku shiga nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zN

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *