Ibtila’i: Kwale-kwale Ya Kife Da Ɗalibai Likitoci A Nijeriya

Wani kwale-kwale dauke da dalibai ya kife a kogin Calabar-Oron a jihar Cross River da ke kudu maso kudancin kasar.

Alfijir Labarai ta rawaito Gidan talbijin Kasar NTA, ya bayyana cewa kwale-kwalen yana dauke da daliban da ke karatun aikin likita 14 yayin da ya kife.

A sakon da NTA ya wallafa a shafinsa na Twitter ranar Asabar da tsakar dare ya ce daliban, karkashin kungiyarsu ta NIMSA , sun je Calabar ne a wani bangare na bikin da suke yin shekara-shekara amma sai suka yanke shawarar shiga kwale-kwale don kashe kwarkwatar idanunsu a wurin shakatawa na Calabar Marina.


Sai dai “abin takaici shi ne kwale-kwalen ya kife” amma dalibai 14 sun yi sa’a bayan da jirgin rundunar sojin ruwa na kasar, wanda ke kusa da su a lokacin, ya yi gaggawar ceto su.

Amma har yanzu ba a ga dalibai uku ba kuma ana ci gaba da nemansu, a cewar NTA.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook.   Alfijir Labarai
YouTube.     Best Seller Channel
Twitter.        @Musabestseller
Instagram.  @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai  👇

https://chat.whatsapp.com/GdLiqZyHuSz5NhjdGoGRGZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *