Hukumar DSS Ta Magantu Akan ICPC, CCB Da Kuma Abdul’aziz Yari

Kakakin Rundunar ‘yan sandan sirrin ta ce zargin ba shi da tushe na gaskiya ko kuma sahihanci kuma hasashe ne na masu kirkiro.

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta ce jami’anta ba su kai samame a ofisoshin hukumar yaki da rashawa mai zaman kanta (ICPC) da kuma Code of Conduct Bureau (CCB) ba.

Rundunar ‘yan sandan sirrin ta kuma ce babu wani fayil da aka kwashe daga hukumomin gwamnati guda biyu kamar yadda wasu kafafen yada labarai suka yi ikirarin ba.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, kakakin hukumar DSS, Peter Afunanya, ya kuma ce rahotannin da ake yadawa cewa hukumar ta yi wa alkalan kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa karya ne.

Hukumar ta DSS ta ce zarge-zargen ba su da tushe na gaskiya ko kuma sahihanci, kuma hasashe ne na masu kirkira

“Don daidaita bayanan, DSS ba ta aiwatar da kowane irin aiki a ICPC da CCB ba ko cire fayiloli daga ofisoshinsu,” in ji sanarwar.

“A bisa koyarwa, hukumomin biyu, da kansu, sun karyata labarin a cikin sanarwar manema labarai da aka yada.”

Rundunar ‘yan sandan sirrin ta kara bayyana a matsayin abin dariya, rahotannin da ke cewa hukumar DSS ta gayyaci tsohon gwamnan jihar Zamfara, Abdul’aziz Yari saboda ya ki amsa kiran wayar shugaba Bola Tinubu.

“Yari ya san dalilin da ya sa aka gayyace shi,” in ji kakakin.

“Ayyukanmu za ta kasance masu mai da hankali, juriya, kishin ƙasa da nuna ƙwarewa wajen gudanar da al’amuranta.

An umurci jama’a da su yi watsi da labaran da ba su dace ba wadanda ke da nufin haifar da rashin jituwa a cikin kasar da kuma bata wa shugabancin hukumar.”

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Alfijir Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/GdLiqZyHuSz5NhjdGoGRGZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *