Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutin Hutun Maulidin Annabi S A W

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Laraba 27 ga Satumba, 2023 a matsayin ranar hutu maulidi na bana.

Alfijir Labarai ta rawaito hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren ma’aikatar harkokin cikin gida, Oluwatoyin Akinlade, ya fitar a ranar Litinin.

Sanarwar ta ce ministan harkokin cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ya bukaci ‘yan Najeriya da su kasance masu hakuri musamman a wannan lokaci, tare da koyi da halayen shugaba Annabi Muhammadu Sallahu alaihi wasallim

“Ministan ya taya daukacin al’ummar musulmin gida Nigeria da na kasashen waje murnar bikin maulidin na bana.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/FNim39ly65N2CzcTt8FgWb

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *