Gwamnan Kano Ya Jagoranci Ragargaje Wasu Gine-gine Da Akayi Ba Bisa Ka’ida Ba

Alfijr ta rawaito Gwamnan jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf da sanyin safiyar Asabar ya kaddamar da fara rusa shaguna da gidajen da jama’a suka yi i ba bisa ka’ida ba.

Rahotanni sun nuna cewa wani gini mai hawa uku mai shaguna 90 a kan titin fiilin Sukuwa, an tuguje shi da misalin karfe 2:00 na ranar Asabar.

Gwamnan wanda ya jagoranci aikin rusa ginin ya samu rakiyar kwamishinan ‘yan sanda, Muhammed Gumel.

Idan dai za a iya tunawa Abba Kabir Yusuf bayan zaben sa, a matsayin zababben gwamnan jihar ya yi barazanar ruguza gine-gine a jihar kan kadarorin jama’a da akayi ba bisa ka’ida ba.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu aFacebook. Alfijr Labarai YouTube. Best Seller ChannelTwitter. @MusabestsellerInstagram. @musa_bestsellerKo a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇https://chat.whatsapp.com/GdLiqZyHuSz5NhjdGoGRGZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *