Gwamnan Jihar Kogi Ya Kori Kwamishina Da Wasu Mataimakansa

Alfijir Labarai ta rawaito Gwamna Yahaya Bello na Kogi ya kori kwamishina da wasu mataimaka biyu a ranar Talata

Gwamnan ya kori kwamishinan noma na jihar, David Apeh.

Haka kuma an kori mataimaki na musamman ga gwamnan kan harkokin bada agajin gaggawa, Mista Danladi Isah-Yunusa, da Hajiya Maryam Salifu, shugabar hukumar kula da gidajen otel da yawon bude ido ta jihar Kogi.

Korar mutanen uku na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakatariyar gwamnatin jihar, Misis Folashade Ayoade-Arike, ta fitar a Lokoja ranar Talata.

Ko da yake ba a bayar da dalilin korar Apeh ba, Ayoade-Arike ya ce gwamnan ya amince da dakatar da nadin nasa nan take.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Alfijir Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/GdLiqZyHuSz5NhjdGoGRGZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *