An Ƙaddamar Da Na’urar Hana Yara Bacewa A Masallatai Masu Daraja

Alfijr ta rawaito babban Limamin Harami Sheikh Sudais ya kaddamar da wata na’ura wadda za ta taimaka wajen hana yara bacewa a masallatai masu daraja Ka’aba da na Annabi a ranar Laraba.

An samar da Na’urar ne don samar da wata takardar shaida da za a rinka makalawa a hannun kanana yara a duk lokacin da za su shiga daya daga cikin masallatan.

An kuma bayyana cewar za a rubuta sunan yaro da kuma lambar wayar iyayensa a kan takardar, wanda hakan zai bayar da damar kiran iyayen yaro da zarar ya bace ko wani akasin.

Bayanai sun nuna yara da dama na bacewa a cikin jama’a a masallatan Ka’aba da na Annabi saboda yawan mutanen da ke ziyartar masallatan domin ibada.

📸 – Haramain Sharifain

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Alfijr Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/G1wNveF9mGU7jec5mWhFvZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *